30/05/2026
Ma'aurata Ne Kawai Zasu Ce Wani Abu Anan...
Wannan matar ta kawo ƙorafi da neman mafita. Ku karanta labarin nan nata gaba ɗaya domin bata shawara, amma don Allah banda zagi domin ba wanda yake wuce ƙaddararsa.
Ta ce, "Mun fi shekara bakwai da aure da mijina. Muna da yara uku. Kullum cikin soyayyar juna muke, ba zan ce bamu taba samun saɓani ba, amma dai irin wanda sai an shiga tsakaninmu bamu taɓa samu ba. Ban rasa kowacce irin kulawa ba, abinci, kwanciyar aure, hakuri da juriya kulawa har irin wasan soyayyar nan.
Sai dai...
Ma'aikaci ne a Abuja yake aiki idan ya tafi yakan kai wata biyu zuwa uku kafin ya dawo. Yana da aboki wanda ya aminta dashi idan baya gari shi yake zuwa yakai yaransa a Makaranta. Wannan ne yasa shaidan ya rinjayemu muka fara soyayya har ta kaimu ga..
Wata rana mijina ya dawo daga tafiya da wata tsaraba ta musamman domin ya min bazata, amma kash.... Ni nayi masa bazatar da har yau zuciyarsa bata daina bugawa ba. Shigowa yayi ya same ni da abokinsa a kan Gadonsa muna aikata....
Daga wannan rana duk wani farin ciki yayi ɓatan dabo a Gidana 😭 Na rasa ƙima, daraja, da nutuswa yarana ma basu san me yake faruwa dani ba sai dai nayi musu ƙaryar banida lafiya.
Mutumin nan bai sake ni ba, bai ƙaro aure ba kuma baice na tafi Gidanmu ba sannan bai faɗawa kowa ba. Amma har yanzu maganar nan da ake shekara kenan bai sake yi min magana ba, baya cin abincina baya magana dani.
Wallahi ko baƙi bana so nayi domin gani nake zasu gane komai don na canja na rame gaba ɗaya k**ar mai ciwon Hiv.
Don Allah ku bani shawara tayaya zan dawo, mu zauna lafiya k**ar a can baya? Na shiga uku.
_____
Wannan shi ne, don Allah ku bata shawara banda zagi. Ba wanda yafi ƙaddararsa, ita ƙaddararta kenan. 🥺