Dandalinyunusakabo online

Dandalinyunusakabo online Allah baya son zalnci

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya karɓi dan majalisar dokokin Jihar Kano mai wakiltar mazab...
02/06/2026

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya karɓi dan majalisar dokokin Jihar Kano mai wakiltar mazabar Makoda, Hon. Muhammad Ahmad Tomas, wanda ya sauya sheka daga jam'iyyar NDC zuwa APC.

Hon. Tomas, wanda a baya ya sauya sheka zuwa jam’iyyar NDC, ya sanar da komawarsa APC ne yayin wata ziyara da ya kai gidan Sanata Barau a Abuja ranar Litinin, tare da rakiyar shugabannin kananan hukumomin Makoda da Dambatta, Alhaji Isa Currency da Alhaji Jamilu Abubakar Dambatta.

Yayinda yake karbar Dan Majalisar, Sanata Barau ya bayyana cewa wannan sauyin wata alama ce ta yadda siyasar Kano ke sauyawa, musamman yayin da ake tunkarar zaben shekarar 2027

02/06/2026
Gwamnatin Najeriya na ci gaba da fuskantar matsin lamba kan gaza kuɓutar da ɗaliban makaranta 42 da aka sace a jihar Bor...
02/06/2026

Gwamnatin Najeriya na ci gaba da fuskantar matsin lamba kan gaza kuɓutar da ɗaliban makaranta 42 da aka sace a jihar Borno da har yanzu ke hannun ƴanbindiga.

Iyayen ɗaliban sun bayyana fargaba cewa kamar gwamnati ta manta da ƴaƴansu, saɓanin irin matakan da suke jin ana ɗauka a jihar Oyo na ƙoƙarin ceto ɗaliban da aka sace.

Sai dai tuni mai bai wa shugaban Najeriyar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Abdulaziz Abdulaziz ya musanta zargin da iyayen ɗaliban jihar ta Borno s**a yi.

Yaran dai sun shafe kwana 17 a hannun ƴanbindiga tun bayan sace su a garin M***a a ƙaramar hukumar Askira Uba.

Dakta Chi Namke shugaban al'umma ne a yankin ya shaida wa BBC cewa suna cikin tashin hankali kasancewar yaran da aka sace ƙanana ne.

"Daga gwamnatin Borno, akwai kwamishinan ilimi da ya zo amma daga wajen gwamnatin tarayya ba mu ga ko mutum ɗaya ba," in ji Dakta Chi Namke.

A cewarsa, irin haka tana faruwa a wasu jihohin kuma gwamnatin tarayya tana aika tawaga domin jajanta musu.

Ambasada Ahmad Shehu, shugaban wata gamayyar ƙungiyar farar hula a yankin arewa maso gabas ya ce haƙƙin gwamnati ne ta gaggauta ceto ɗaliban.

"Da aka yi na M***a, ya faru a jihar Oyo a lokaci ɗaya, namu ba abin da aka yi, sai wancan kuma gwamnati ta ɗauki mataki." in ji shi.

Ya ƙara da cewa "shugaban ƙasa ya buƙaci manyan jami'an tsaro da su tare a jihar Oyo domin ganin an kuɓutar da yaran da aka sace.

Fadar gwamnatin ta bakin Abdulaziz Abdulaziz dai ta danganta iƙirarin iyayen ɗaliban jihar ta Borno da shelar ƴan adawa saboda a cewarsa shugaba Bola Tinubu yana ƙoƙari ya ga an yi abin da ya dace domin kuɓutar da ɗaliban.

A yau Talata ne ƙungiyar ƙwadago ta malaman makaranta NUT za ta jagoranci zanga-zanga a sassan Najeriya domin tilasta wa gwamnati ɗaukar matakan gaggawa na ceto ɗaliban.

On Monday, June 1, 2026, I received the leadership of Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) Kano State Ch...
01/06/2026

On Monday, June 1, 2026, I received the leadership of Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) Kano State Chapter, led by Professor Abdullahi Saleh Pakistan, on a courtesy visit.

During the meeting discussions focused on issues relating to the development and progress of Kano State, as well as ways to strengthen cooperation in advancing the state's socio-economic and religious objectives.

Speaking on behalf of the delegation, Professor Abdullahi Saleh Pakistan expressed appreciation to the Kano State Government and conveyed the organization's gratitude to His Excellency, Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, for the Hajj slots allocated to JIBWIS, describing the gesture as a demonstration of the administration's commitment to supporting religious organizations and promoting the welfare of the people.

-MSG

APC ta dakatar da ɗan majalisar tarayya da wasu manyan masu mukami kan yiwa jam'iyyar zagon ƙasa a JigawaJam'iyyar APC a...
01/06/2026

APC ta dakatar da ɗan majalisar tarayya da wasu manyan masu mukami kan yiwa jam'iyyar zagon ƙasa a Jigawa

Jam'iyyar APC a jihar Jigawa ta dakatar da ɗan majalisar tarayya da Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma da wasu manyan jiga-jigan jam'iyyar guda shida kan yiwa jam'iyyar zagon ƙasa a jihar Jigawa.

Da yawa daga cikin Yan'Nigeria basuki ace na mutu ba.Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu.
01/06/2026

Da yawa daga cikin Yan'Nigeria basuki ace na mutu ba.

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu.

Ku faɗa masa ni ma na ce da shi yaro - Martanin Comr. Aminu Abdussalam Gwarzo ga Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf.Me za ku ...
01/06/2026

Ku faɗa masa ni ma na ce da shi yaro - Martanin Comr. Aminu Abdussalam Gwarzo ga Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf.

Me za ku ce?

'Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojojin Nijeriya Da Matarsa A KatsinaDaga WakilinmuWasu da ake zargin 'yan bindiga ...
31/05/2026

'Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojojin Nijeriya Da Matarsa A Katsina

Daga Wakilinmu

Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun yi garkuwa da tsohon Kakakin Rundunar Sojojin Nijeriya, Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, tare da matarsa a garin Matazu da ke Jihar Katsina.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar yayin da tsohon jami'in sojan da matarsa ke kan hanyarsu ta zuwa birnin Katsina.

Majiyoyi sun bayyana cewa maharan sun tare motarsu ne a kan hanya kafin su yi awon gaba da su zuwa wani wuri da har yanzu ba a tantance ba.

An kuma ruwaito cewa direban tsohon kakakin sojojin ya tsira daga harin, sai dai maharan sun harbe shi da bindiga yayin da suke aiwatar da satar.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, jami'an tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan faruwar lamarin ba, kuma ba a samu karin bayani kan halin da wadanda aka sace suke ciki ba.

Ana sa ran hukumomin tsaro za su fara gudanar da bincike domin ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kamo wadanda s**a aikata wannan danyen aiki.

Shugaba Tinubu ya amince a baza jami'an tsaron gandun daji guda 1,000 da jami'an tsaro domin ceto dalibai da malamai da ...
31/05/2026

Shugaba Tinubu ya amince a baza jami'an tsaron gandun daji guda 1,000 da jami'an tsaro domin ceto dalibai da malamai da aka yi garkuwa da su a Oyo

Mai bai wa Shugaban Tinubu Shawara kan yaɗa labarai Bayo Onanuga ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa wata babbar tawaga ta gwamnatin tarayya ta isar da umarnin Shugaban ga shugabannin al’umma da ‘yan majalisu yayin wata ziyara da ta kai ƙauyukan Esiele da Yawota da ke ƙaramar hukumar Oriire a ranar 31 ga Mayu, 2026.

Babban alkalin kotun tarayya ya sauya alkalin da ke sauraron karar da tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar ADC na kasa, ...
31/05/2026

Babban alkalin kotun tarayya ya sauya alkalin da ke sauraron karar da tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar ADC na kasa, Nafiu Bala Gombe, ya shigar yana kalubalantar shugabancin jam’iyyar karkashin jagorancin Sanata David Mark.

Rahotanni sun bayyana cewa an mayar da karar gaban Alkalin Kotun Tarayya, Peter Lifu, domin ci gaba da shari’ar.

Tun da fari dai Nafiu Bala Gombe ya neman kotu ta hana Sanata David Mark, Rauf Aregbesola da sauran mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar gudanar da harkokin shugabancin ta, yana mai cewa nadin nasu ya saba wa kundin tsarin mulkin jami’iyyar ta ADC Dandalinyunusakabo online

Address

Kano
Dal
221

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dandalinyunusakabo online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category